Breaking News

TUMFAFIYA 29

 


 

ZAINAB IDRIS MAKAWA.

[1/30, 7:07 AM] +234 701 497 9567: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA SIRIN KI     SAI ALLAH  ,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2️⃣9️⃣

ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,

 

Tafe suke ba wanda ya iya magana a cikin su don kowasu zuciyar shi a jagule yake lokacin don abinda malamin ya fada masu game da tafiyan nasu.

    Wani unguwa mai nisan tsiya can suntubawa fita gari wurin wani tsohon bafilace suka fito wanda akace ya shahara da asirin mata ko wani iri mace ke so idan taje wurin shi tagama samun bukatanta don mutumin ya iya aiki sosai a cewan manyan matan gari.

    Saidai su tafiyan nasu ya daure masu kai sosai matuka don kusan amsan shi daya da babalawon data taba zuwa wurin shine lagos a baya ita da kawarta dan sanyin da taji shine zancen hjy karima daya fada mata cewa ba zata taba haihuwa a gidan Abba ba asalima dai baiga zama a tsakanin su ba nai tsawo a duban shi din.

   Wanan ya dan sa ta rage jin tafasan zuciyar ta a lokacin saidai tunawa da zancen zahra din yasa kuma taja tsuki a lokacin da bata shirya jan hakan ba a bakinta.

   Kallon ta yar nata dake gefen mai zaman baza tayi tana fadin mekuma kika tuna kike jan tsoki nifa dama damuwa kan wanan tsohuwar da Alh ya kwasone don sam ban damu da zancen yar nan taku ba.

   Don nasan bata taba kai diyan ki kaf dinsu a duniyan nan don me zaki saka damuwa haka akan yarinyar nan ne wai maimuna ?

   Yarinyar da duk inda kikaje akece maki akwai matsala a rayuwan ta tome ya rage kuma ki mata yanzu ki barta can suji da matsalansu ita da uwarta su hakan ya shafa ai.

   Watau ya saude baki ganewa ne tunda nasa ido ga yarinyar nan zahra naji Allah ya saka min tsanarta tun tana karamar ta kwata kwata na tsani yar a raina wallahi.

  To ya zakiyi tunda mai hadawa ya hada zaman ku a innuwa daya saiki kawar da idonki a kanta ki mayar da ita da banza duk daya a gareki kiba kanki lafiya zaifi.

    Ko nace zanyi hakan na kwatanta yadda uwarta ke taushe zuciyar ta wurin nunawa nawa diyan kauna sai naji na kasa hakan ga duk yaran salma din .

   Bana son naga Alh yana nuna masu kulawa ko wani nuna kaunan suma diyane a gareshi don Allah ya gani banso ace wai salma ta haihu da Alh ba a gidan nan.

    Haka da yawa suke ji kan yayan mijinsu saidai kowa na taushe zuciyar shine a zauna lafiya bakiji manya sunce dan kishiya rikon mai hakkuri ba .

    Duk wacce kikagani tana ji da dan kishiya dole akwai tabon haka a zuciyan ta yan kadan ne keyi tsakani da Allah to ita taki mun kasa gane ko a wani ajin take do  komai wayaun ka baka taba fahintar salma.

    Munafuskace ta gaske don baka taba ganin bacin ranta kome kuwa zakai mata zata iya hadewa ta shanyewa cikin ta ta boye abin yai mata zafi koda kuwa mijin ne yai mata hakan.

  Ai taci sunan ta kuwa salama son sunan ya dace da halinta mama saude ta fada a hankali taga yar uwan na rage gudun motarsu taga tayi parking a wajen masu kayan marmari zata saya.

   Tana tsayawa masu kayan marmarin suka taso suna fadin hjy a sai kankana asai abarba wani kuma na fadin hjy Apple ne ko kai don Allah wancan nake so na tsaya ta fada a dan tsawace masu tallan suka fara ja da baya mai table din lemun ya taso yana dauko leda tare da fadin na nawa za a zubane ?

    Zuba na dubu daya sai Ayaba shima na dubu daya ta duka tana dauko kudi a jakkan kayanta tana dagowa idonta ya sarke cikin na wani makaho dake zaune rike da sandanshi baiwa kowa a wurin magana sai dai mika roba da yakeyi.

   Da sauri ta kawar da kanta gareshi don sai halittan mutumin taga ya bata tsoro kafin ta dago kai da niyar bawa mai kayan marmarin kudi sai ganin shi tayi bakin window motan tsaye yana fadin.

    A taimaka saboda Allah da Annabi matafiya Allah ya sauke lafiya tafiyan da akayi Allah ya mayar da aniya ga mai ita sarkin da akayiwa ya sani.

   Masu mugun nufi ya koma masu masu hassada halinsu ya bisu masu, , , haba malam muba tafiya muka fito ba nan cikin gari muke mama saude ta fada a hasale don irin adduan da taji yana fita a bakin shi.

   Mai sayar da kaya  marmarin yace dasu ai malam mamman kalar baranshi ke nan shi hjy ai fata na gari yai maku yanzu din Allah ya kaiku gida lafiya.

  Motar mama data fara jan motan tayi yasa ya kauce yana masu Allah ya tsare ya bar wurin yana binsu da kallo har suka bacewa ganin shi ya koma bakin sana,arshi.

   Mama saude ta fara magana tana fadin kinji mun mutumi wazai baka sadaka da wanan baran nasa wai nufin mutum ya bishi kamar wanda yasan abinda muka fitoyi.

  Nima shinake tunane mama ta fada irin mutanen nan ina tsaron haduwa dasu don wata kawata a lagas ta taba yin gamo irin haka da kyat ta sha daga sherin su.

   Sai yamma sosai suka isa gida suna magana daya sun shiga gida ana kiran magariba direct part dinsu suka nufa mai wanki yana biye dasu da kayan tsaraban da suka sayo a hanya.

    A sabule ya shigo gidan Dije dake zaune a baki  murhu ta dago ta dan kalleshi tana fadin yau da wuri haka ka dawo yace eh Dije yau munje kauyene na dauko hatsi a can .

    Ledan da ya shigo dashi a hannun shi ya aje a gaban ta yana fadin wanan naman na gani a can yai min araha na sayo muna shi kinsan kauye suna da arahan komai su.

   Ledan ta jawo zuwa gabanta ta fara buda tana fadin kace min dai yau dadine a gidan mun huta da cin yan yama yama kwana biyu gata nan dai ki zuba ma,ishi kowa ya wadata yaci .

  Mikewa yayi ya nufi wurin garke yana gyara masu dauri kafin daga can din yace Dije uwargarke dai ta barmu da kewan ta kullun nazo wurin nan saina tuna da ita wallahi.

    Dole a tuna da uwargarke sabo ba karamin abu bane don kusan shekara nawa ana tare da ita ba zan manta ba a daren da mahaifinka zai tafine yazo gidan nan sallaman ka shine ya bani fam biyar nayi ta boyonsu har suka kara taruwa.

   Saina hada na fara sayan karo dashi ina dan kiwatawa sai na sayar nasai wani har kai ga sayo uwargarke daga baya naji bazan iya sayar da ita ba don tana da shigan ciki a jikinta lokacin.

    Kai kuma ka dauki son duniya ka dora a kanta ance dabba baya dadewa to nidai kan uwarharke tayi min halarci don ta haifa min diya da yawa inba daga bayan nan da ta zama juya ba ta daina haihuwa nasan kuma tsufane tayi ya jawo hakan.

   Yanzun gashi ta barmu don kanta tayi tafiyanta ai mun morewa wanan dabban sosai ko yanzu ta barmu ai munci ribanta ko.

  Ballema bata tafi ba duk inda take idan ba yankata maishi yayi ba zata dawo gidan nan in sha Allahu komai daren dadewa kuwa nasan zata dawo garemu.

   Sororo Dije tayi da ledan data dauka wanda ya shigo dashi da nama zata ta wanke tace haba dai Amadi har son da kakewa uwargarke yakai haka yau kwana nawa da batan ta inane ba ace min anganka kana nemanta ba ?

   Ni kaina na zaga kaf gidajen unguwan nan na duba koda wanda ya ganta amma babu labarin ta ai ya kamata ka hakkura haka ka fitar da rai a zancen ta kuma.

    In sha Allahuma zata dawo don na yarda da hakan kuma an fada min hakan ma zai faru daga inda take takemai kallon kanka daya kuwa Amadi ya gane me take nufi yace .

   Dije uwargarke da kike gani alherice a garemu rabuwa da ita kinga zai muna jimame din haka kiyi fatan Allah yasa ta dawo gidan nan garemu.

    Ta dawo wani gida koka manta cewa a yanzu ita din ba mallakinmu bane wai da me itafa a yanzu don me zaka dauki sin duniya ka dora a kan dabba haka wai ?

   Murmushi yayi daga duken da yake yana fadin keba zaki gane hakan ba ai Dije amma nasan abinda nakeyi ni tace to Allah ya kyauta kada ka koma dan bautan akuya na mutanen kasan India.

   Suda kiri kiri zasuga ta mutu su nemi wata suna mata bauta kuma daga baya ko su gina gunkita su dinga bauta mata.

    Dariya ya kwashe dashi ya gama gyara  gida ya koma gyaran wajen gidan su ya dade a can wajen yana gyara kafin ya shigo cikin gidan ya samu harta gama girki tana kokarin gyaran wurin.

  Karban aikin yayi daga hannun ta koma kofan dakinta ta zauna tana fadin yaro da iya aikin mata haka matar ka ta huta saika dinga miya ita tana tuwo ke nan.

  Daga duke ya bata amsa yana fadin dukama zanyi mata ita ta huta kina ma zancen mata wa zai bani yarsa garin nan an fara fada min cewa banda asali.

 Wane dan banzan ya fada ma hakana wani irin zancene haka nake ji a bakinka kai mutane akwai iya sheri garesu kaida ubanka ya bar garin nan yatafi ya barka a saman kafafun ka biyu.

   Amma aiku kuka hana inna tabishi yanzu ba gashi ta zauna garin ba da kunka hana tabin mahaifina ai kun yarda tabi wani daga baya kuma.

   Kai Amadi shin kanka daya kuwa a gidan nan koka fara shaye shayen zamanine da akeyi yanzu a a zan bar yata zuwa wani nisan uwar duniya da banda kowa a can ni ina nan cikin gusau zaune zama ?

   Ashe dama ni kaka zargi da hanaka zama da mahaifin haka kawai nika daukan yata in mikata uwar duniya ni ina nan nan niya gara dai su rabu din yafi min sauki da ace ya tafi da ita can inda ba a sani ba.

   Kina fadin wai ba a sani ba baku san garinsu ba kuka yarda yarku ta aureshi dole inga laifin ku a yanzu don na daina jin zafin mahaifina da nakeji a baya yanzu laifin ku nake gani.

   Shiru tayi tana bin jikina nata da kallon mamaki kafin tace shiyasa kataho min da zancen shi kwanaki ko ai tun lokacin na fara zargin da akwai wani magana a kasa da kake son fito min dashi.

    To bari kaji garin nan kaf ba wanda naji ya taba zuwa garin da yace ya fito saidai naji sunan garin a gidan redio jefi jefi.

    Amma dai ai cikin kasan nan yake ko koma ba kasan nan bane ya zama dole yanzu inje neman mahaifina duk da yayi banza dani nan cikin duniya amma nasan dole ina ranshi idan yana raye.

    Wa hwada maka ga garin da yake da zama taka maimai ko nan daya taho ai a karkashin Alh Abu dan canji ya zauna shina ma yayi auwalin aurene har muka yarda muka bashi ita.

   Daga baya da tahiya tayi nisa yake fada muna shima bai san garin su ba ya dai yaba da hankali nena ya tsaya mashi akai auren.

    Gara ma tun wuri ka fitar da zancen shi a ranka don kila ma baya raye yanzu ni haka nafi sawa raina don gaskiya inda Auwalu na raye nasan daya taho nan ko don kai.

   Dije ko bai raye zanje yan uwanshi su san dani a a nika zama nan ana tsangwamata kan laifin da ban aikata ba gara naje nasan asalina da anka fara fadin bani dashiya.

  Aiki ko ja a gabanka zuwa wanan garin har uwar duniya don baka san iya kwanakin da zakayi a hanya kafin ka kai garin.

  Zuwa lokacin yagama hasala da kakar tasa don da ace Dijen tasan yadda zuciyar shi ke tafarfasa a lokacin da bata yi wanan zancen dashi ba a lokacin.

   Damace gareshi a yanzu don haka bai cewa Dije din komai sai shirin tafiya daya fara bayan ya tambayu kan yadda zai kai kanshi garin mahaifin shi na asali.

   Tare da samun karin bayanin yadda zai iya gano mahaifin nasa idan ya isa wurin wasu abokan hurdan mahaifin nasa a nan gusau da yai zaman mutunci dasu a garin.

   Sallah asuba nayi na zauna ina tulawa a wurin kafin gari ya kara haskawa na fara jin motsi a gidan na mutanen gidan dake kara kaina a tsakar gidan ina jin motsin duk abinda sukeyi saidai ban fito bane waje lokacin.

    Bayan na shafa na mike na shiga bandaki wanka nayi don nayi saboda hakan don zuwa school dana saba fita da safe dana gama azzakar saina mike na shiga wanka.

   Na fito na shirya cikin dinkin atampa da akai min buje da riga na fito yar shar dani na mike na fito zuwa falon gidan namu.

    Babu kowa a falon saidai abinci da yan aiki suka jera a saman dining wata kafira da dan bujene a jikinta ta fito daga kitchen dauke da wani katon dood warmer a hannun ta tanufi dining din ta aje ta juyo sai lokacin ta ganni a zaune.

  Ina kwana mah ta fada tana dan rage tsawonta kadan don ban girma a gareni na amsa ina kare mata kallo tare da kyaman yadda na ganta nasan ba musulma bace.

  Don mu a lokacin zaman mu gidan ummah bata taba yarda ta dauki yar aiki kafira ta jefa cikin mu saidai musulma yar uwan mu da zata bamu tarbiya a tarevta dauketa tankar yarta na cikinta.

  Idan zasu tafi kuma a rabu a cikin mutunci da dadin rai ana kewan juna kamar kada su tafi amma gashi yau arniyace a gidan take dan yawo da buje kuma cikin kazanta haka irin nasu ko don ina kyaman hakane a raina bansani ba ?

  Hjy nakawo maki abincin ki a nan ne ta tambayene cikin girmamawa nace no ki barshi idan na tashi ci zan nemeki tace yes mah ta nufi kitchen inda suke aiki.

    Daga kai nayi na kalli dakin ummah wanda a yanzu mallakin mommy ce wai sai naji zuwa Abujan nan ya zame min dana sani don abin bakin cikin da nake gani a gidan ga zuwana.

   Karan budan kofa naji yasa na dago kai mommyce tafito daga dakinta tana kokarin nufar dakin Abba dake rufe sai kuma ta juyo ta dawo zuwa dining da nufin duba abinda aka girka na breakfast.

    Kullan farko ta bude ta rufe ta fara kwalawa kiran sunan wata da Tabitha daga can kitchen mai sunan ta amsa sai gata da sauri hjy ta fara fadin banace idan kun gama ku fada min kafin ku kawo kitchen wai meyasa ku bakwa jin magana ne ko koyaushe sai na dinga nanata maku hakan ne ?

  Dauki kikai min daki idan na gama zan kiraki fito dashi sorry ma Janet naba ta kawo ashe nan ta aje ai ban manta da dokanki ba.

  Common dauki ki tafi kin tsaya kina surutu tana fadi ta juya ta shige daki matashiyar matan tabi bayan ta duk wanan abin bata kula da cewa ina falon zaune ba ta shige dakin.

  Gabana ne ya fadi me za a jeyi da Abincin kuma a dakin mommy tsam na mike daga inda nake zaune din na nufi dakina dana fito gado na haye na kwanta ina faman tunane.

    Barcine ya soma daukana a hakan naji an turo kofa na bude idona mommyce  tashigo a cikin shirin ta na fita aiki ganina na shirya tsam kamar mai shirin fita ta saki murmushi a fuskanta tana fadin.

   A, a my daughter wanan kwalliyan haka rangas ko wani wurin zaki tafi dagowa nayi da dan murmushi a fuskana na zauna ina kokarin sauka daga gadon tare da fadin ina kwana mommy ?

   Lafiya kalau ya gajiyan hanya koda yake da alama kin sauke gajiyan ma ai tunda naga harkin shirya haka fita zakiyine ta sake tambayana.

   A, a mommy ba inda zani kawai dai haka na saba dashi damani na fada na koma saman gado na zauna tace to ai hakan yai min dadi sosai don dama ga abinci can an gama sai ki fito muci kafin Alh ya fita dama baku wani gaisa sosai ba jiya ya shige part dinshi.

   Mommy bana karyawa da safe haka sai dai in an jima zan fito nace wajajen karfe goma kice min yar tawa baturiyace kema kina irin tsarinsu ke nan dai ?

   A a mommy haka dai na saba daman ni to ki fito ku gaisa da Abbanki yana falo zaune zan fada masu kadasu kwashe kayan abincin sai idan kin karya din yanzu taso muje kafin ya fita.

  Zaune Abba yake yana waya tana fitowa yake fadin kinsan fa sauri nakeyi kin kuma je kin zauna abinki can  sai gani na fito bayanta hakan yasa yai shiru a lokacin.

   Har kasa nakai ina fadin Abba ina kwana lafiya ya amsa min dashi yace ya gida ya kika barsu a can , ?

    Kowa lafiya suna gaida ku  amma ban samu zuwa gidan hjy na sallameta ba don nasan zai tambayeni hakan.

    Ba laifi ya fada yaci gaba da cin abincin shi da mommy din ta zuba mai wanan din kuma datasa akai mata daki dazun.

  Ta juyo tana fadin daughter idan kinzo karyawa wanan ferfesune a cikin cooler zakiji dadim shi sosai ga Abban kinan ma zai sha kefa Abba ya fada naji tace ai kasan ban faye cin kifi haka da safe ba.

  Kofa aka bude wasu mata biyune suka fito a cikin shirinsu duk muka dago muna kallo  su .

 

No comments