Breaking News

TUMFAFIYA 4

 


_Gefe d'aya zafafan kayan gyaran HQ kala kala Wanda zasu ciko ki su matseki Gam sannan subaki ni'ima da dandano irin wanda akeso ,hmmm kedai ziyarci maman yusuf sokoto Dake marna Police station ko Kuma ta numbar wayarta Kamar Haka 08133079957 ko Kuma 07069711327 don bambance tsakanin Aya da tsakuwa , zamu aika maki da kayanmu a duk inda kike acikin fadin Nigeria da Niger harma da wasu k'asashen , cikin aminci da yardar Allah ,karku manta a Dade anayi sai gaskiya_💃🏻💃🏻💃🏻💥💥

 

_Hmmmmm in Ana Dara fidda uwa ake ,har Ila yau darajar wannan watan min fito maku da wani mashahurin set Wanda Zaki samu kalolin Kaya aciki masu dauke da sirrikan mallaka , gefe daya ga hatsabibin turaren mallaka ,Wanda ba namijin da zai jishi hankalinshi Bai tashi ba duk acikin wannan set namu Mai suna *MUJALLAB* wannan mashahurin set a waje biyu kawai kike da damar samunshi , Zaki iya samunshi a wajena anan sokoto kenan ko Kuma a jahar Kano wajan Mom fu'ad wadda aka fi sani da gidan k'amshi, Wanda Zaki iya nemanmu ta wannan Numbers_

👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

08133079957 mmn Yusuf sokoto (likitar Mata)

 

 08132506044 Mom Fu'ad Kano (gidan k'amshi)

 

Zaku same MUJALLAB a farashi Mai sauk'i🥰🥰🥰🥰

 

_Amare zawarawa tanadinku daban ne na shirya tsab domin Yi maku hadin *sabon budurci* Wanda Zaki ciko ciki da waje ku hade Gam Gam kamar baku taba sanin wani d'a namiji ba domin kankarowa kanki mutunci da daraja a wajan oga_

 

_Hakama amarenmu Wanda suka samu matsalar rashin budurci sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,naku na musamman ne ,Hadi ne da in akayi makishi da izinin Allah sai kinzo kinamun godiya , kedai nemeni ta pc don samun cikakken bayani akan hakan_

 

*Idan fa nace Zan zayyano maku ire iren kayan da muke dasu to fa wannnan page din bazai ishemu ba ga Maison ganin kalolin kayana yayi sarving number ta yayimun magana nayi nashi zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd*🥰🥰🥰🥰🥰

 

*Pls in ba serious kike ba don Allah ki Bari sai kin shirya siya sai muyi magana azumi ne yanzu banason mu batawa juna lokaci*😊😊😊

 

08133079957

07069711327

Mmn Yusuf likitar Mata

 

 

 To Allah yaba amare da uwargida ikon ganawa da maman yusuf likitan mata yasa a dace da abinda ake nema a wurinta amin gadai hajiya mama ta fara baiya a gidan mayana.

    Maimunatu ina dai lafiya kira haka da wanan uban safiyan haka har kin ban tsoro gaba yana faduwa ina badai wani abin bane yafaru kuma ?

   Tsuki mama din taja tana fadin wallahi wanan banzan hjy kariman tazo jiya ta hanani barci da dadi da wani zance nata mara dadi akan maamah.

    Maamah dai yar nata ta fada cikin tsigan tambaya wallahi wani tuni tayi min kan yarinyar nan wai mun kusa samun sarakai gwanoni ko wasu hamshakai akan maamah din.

    Ai keda bakisan da hakan yana tafe gareku bane kome kike nufi kinsan fa maamah din nan ta faye shegen kyau da daukan idon duk inda ta shiga.

   Aina dauka kin gama da wanan babinko tuntuni don banji kina wanan zancen ba ga mazan yanzu kinsa su da sa ido ga mace mai irin dirin yarinyar nan taku idan bamuyi hankaliba sai kiga tazo tafi su Nana samun daki.

    Don Allah bari maganan nan ina raye har haka zai faru da diyana aikoda sayen miji ake zanje na sayowa su nana mijin da kudina nagani a fada na shiga tsara.

   Nasan zaki iya ai basai kin fada ba to yanzu dai sai na shigo ke nan ko kema ai kin sani tunda har na kiraki don wanan zancen ya tsaya mun a raina sosai wallahi.

   Barin shigo sai mu san yaya za ayi ki dubi hanyata zuwa gobe insha Allahu da sauri hjy maimuna tace anya gobe baiyi nisa ba kuwa dadina dake ke nan yar uwanta fada.

     Sun dai aje nagana zata ganta ko yau ko gobe da haka suka aje wayan suka rabu cewa zata shigo koda zuwa yammane insha Allahu.

    Gari ya haska ummah tashigo dubani ta sameni zaune ina addua take fadin kin kin samu tashi ke nan eh na bata amsa ina gaida ita da kwana ta amsa min tare da tambayana kaina nace da sauki.

    Allah ya kara sauki tayi min tana juyawa sai kuma ta tsaya tana fadin zakiko shiga school yau nace insha Allahu ummah ina mikewa to kifito ki karya da wuri kada ki makara ta fada ta fita.

   Mikewa nayi na nade abin sallah kafin nafara kokarin zame dogon rigan dake jikina ya rage sai dan wandon tie dake daga kasana ban dakin na fada nayi wanka kafin na fito na fara shiri.

    Sannu a hankali naji ciwon kan daya dameni jiya yana dawo min amma haka na daure na nufi wurin ummah dake zaune falo tana sallaman kannena zuwa makaranta.

    Zama nayi kujeran dake gefen wanda mamake zaune na dafe kai banyi magana ba har saida ummah ta fahinci hakan ta dago kai tana tambayana lafiya kike kuwa maa,ma ?

    Kaina dago da idanuwana da sukarine na girgiza kai ina nuna mata kaina da kamar ya tsage don ciwo kanne kuma ya kara tashi ta fada cikin dan rudewa.

     Wanan wani irin ciwom kaine haka ki karya muje asibiti zaifi a dubaki a can tea din da ummah tasa aka kawo min na kasa sha karshe da kuka haka na kwanta kife har ummah ta fita ta kira mai aikinta tabar mata kula da part ta kamani muka fita zuwa asibitin da ita.

    Magani aka bani muka dawo gida mun samu yan gidan sun tashi daga kwana don mama bata da karamin yaron yanzu don haka bata bude part din da safe sai sun shaki barcin su na safe kafin su bude wurin su.

   Ban san ya akayi ba mama taji cewa mun tafi asibiti da ummah sai gata a part din mu tana fada daga dakin nake jiyo muryanta sama sama tana fadin.

  Salma na gane yanzun kina son nuna min bani na haifi maamah ba da har za a kai yarinyar nan asibiti ina gidan nan ban sani ba.

    Nina isa in rabaki da yarki kawao dai ganin yadda ta kwanane kuma lokacin baki tashi ba da safe yasa na dauke ta zuwa asibitin do  kada na katse maki barcin ki.

   Amma ai ciwo ya kauwar da komai ko kedai kin nuna min kece kika haifi abinki kawai yasa kikai min hakana  ko yanzu din dan  murmushi ummah tayi amma bata bata hakkuri irin yadda suka saba ba .

    Ta dai shigo inda nake kwance ta dubeni tayi min sannu na amsa da kyar ta fito tun ina jin muryan su sama sama suna wani zancen har na daina jinsu don barcin daya daukeni a lokacin.

    Yinin ranan yai aikin shi dukda yasan yanayi duk da madam tayi alkawarin ba zata bashi kudin aiki shi ba haka kuma bata bashi abinci amma hakan bai hana ya tsaya yai mata aiki tsakani da Allah ba dan kayan cikin kifin daya gyara ya saka a ledan da abincin nan plate biyu da dayan mai aikin tayi dabaran sayar dana farkon da zai wuce ta diban mashi wani maizafi ya gyara masu ko ina na shagon yaje yayiwa madam sallama ya tafi.

    Karfe shidda da rabi ya iso gidan nasu har lokacin ya samu unguwar a hargitse musanman kofan su da bai samu gyara ba ga ruwa ya jawo shara ya tara a kofan gidan nasu.

  Ya shiga da sallama da ledan abinvin shi a hannu ya karasa kofan Dije dake uwar dakinta tana dan gyare gyare jin sallaman shi yasa ta dakatar da abinda takeyi lokacin.

   Ta dan taso da dingeshi tana fadin Amadi har ka dawo ke nan ya amsa da eh Dije yaya kafan taki yau da sauki ko ya tambayeta.

   Fuska ta da  yamutsa kafin tace Amadi sauki saina Allah tunda ba wani magani nake shaba yanzu ledan hannunshi ya miko mata ya juya kawai zuwa dakin shi tabishi da kallo.

  Kafin ta nisa ta mayar da kallonta ga ledan hannun ta tana mamakin meya riko haka da dan nauyi a cikin ledan tana budewa taga hadaden abincin da suke sayarwane a ciki kulli biyu sai miya da aka zuba mai dabban a cikin bakar leda.

   Shiko yana fita dakin shibya nufa ya kwabe kayan jikinshi ya saka wa yan nan tsofin nasa ya dauki abinda suke gyaran kwata ya fita kofan su da kewayen su ya gyara ko ina a cikkn azama din magariba daya kawo kai a lokacin.

    Kiran farko ya shiga gida ya kwabe wanan kayan dayai aiki dasu ya saka wani tsohon jallabiyashi ya dauki buta yayi alwala ya nufi masallaci duk wana  abinda yake Dije na kallon shi tasan kotayi mai magana miskilacinsa ba zai bari ya amsa mata ba.

  Takan tausayawa rayuwan jikin nata mai rayuwa da gadara kamar dan wani da wata masu fada a gari zakace koshi din dan masarautane shi idan yana rayuwa irin tasa sai ka rantse yana da jinin sarauta a jikinshi.

     Itama alwala tayi ra shige daki don lokacin har sauron sun fara bin kafanta daga inda take zaune din tun fitowan da tayi lokacin daya dawo ya mika mata ledan daya shigo dashi a hannun shi.

    Bayan ta idar ta saka idon shigowan shi duk da tasan ba lalai bane ya shigo a lokacin sai an hada isha,i yafi shigowa gidan don hakane bata damu da dawowan shiba a lokacin.

    Chemist din dan bayaro dake unguwarsu ya nufa inda ya da  hado mashi magani na dubu daya hardana shafawan da Dije tafiso a ciki rashin kudine ke hana ya saya mata har sai ya kare ta koma nema a karshe.

    Yana shigowa dakin nata ya nufa ya aje ledan a gefenta kafin ya samu wuri a gefenta yana kaiwa zaune tare da jingina bayan shi a bangon dakin yana sauke ajiyan zuciya lokaci guda.

    Me kuma na samu dan albarka da alaman yau dai mun wayi gari a cjkin sa,a ga leda shake da abinci har da, , , , 

    Sai kuma ta dakata ganin maganin da tayi ya kwaso mata na ciwon kafanta harda abinda tafi so a ciki man abonoke da take shafe kafan dashi ya bar mata zugi.

    Kai zancena gaskiya maigida kace yau muna cikin falalan ubangijine haka masha Allah a ina wanan alherin Allah ya samu haka ta tambaya tana kallon fuskan shi.

   Ya dan ja tsuki tare da fadin kinsan ai na Allah basa taba karewa a duniya wallahi aikin nan dana tsaya dazun na taimakawa malam tanimu har yasa na makara.

   Ina zuwa jami,a madam ta hauni da sababin nan nata a cikin mutane tana min tozarci a bainar jama,a a nan na samu mai zuciyar tsusayi da imani kawai ta ban abinci da kudi ban santa ba ban ma taba ganin ta a school di  nan ba sai kawai ta bayar wai a kawo min.

    Inji Allah ke nan Dije ta fada idan tayima don ta wullakantaka a idon jama,ane ai hakan ya zama ma alheri don ba duka aka zamo daya ba dama.

    Akwai masu tausayi har duniya ta nade yace kwarai kuwa shine Annah yarinyar da muke aiki a tare tayi min dubura ta sayar da wacan abincin sai ta ban wanan tare da sauran canjina kinga kudin nan ya tura hannu a aljihu ya ciro sauran dari biyun da suka rage ya mikowa Dijen .

  Ido ta zare da sauri tana fadin kudin haka sabbi dasu yace wallahi Dije shine na dauki dubu daya na kaso maki yanzu wurin maganin nan.

   Kaji abin Allah ba Allah mun godema yasakawa yarinyar nan da mafificin alheri yadda ta faranta muna rai Allah ya faranta mata ranta har abada kudi haka masu yawa ?

    Shiru yayi yana tunane a ciki  zuciyar shi kafin Dije takai hannu tana miko mashi ledan abincin a gabanshi ya kalla yana sauke ajiyan zuciya take fadin nasn bakaci komai ba a hakan ko ?

   Banci ba kuma ban dauki azumi ba yau dan ganin zanyi aiki da yawa sai ruwa kawai nasha a can ya fada yana mika hannu ga abincin da ya riga da yayi sanyi ko alokacin.

    Ha yaci abincin duk da yana jin bakin shi babu dadi lokacin ya gama ya balle maganin daya sayowa Dije din ya kora da ruwa yana hamdala kafin ya mike ya fita ruwa ya dinga dibowa a makwabtansu yana cika radunan ruwan su kafin ya dauko na karshe ya shiga bandaki ya watsa ruwan ya fito.

   Dakin Dije ya leka ya samu tayi barci a lokacjn kofa ya jawo mata ya rufo ya nufi nashi dakin bayan ya saka dan abin da suke kare gidashi koda wani zai shigo masu gida da dare zasu iya jin motsin shi don barawo bai raina abin sata don an taba shiga masu aka sace wa Dije din tukunyar ta babba suna barci tun wanan lokacin suke rufe kofan gidan nasu.

   Washe gari kiran farko ya samu matashin saman abinda yake sallah mikewa yayi yakara zagayawa bandaki ya dauro wani alwalan daga nan ya kwankwasawa Dije kofa daga ciki ta amsa da gyaran murya yagane cewa ta tashi ke nan a lokacin yasa kai ya fice daga gidan.

   Babu kowa sai wani dattijo dake nafila shima nafilan ya fara kamar yadda dattijon daya sama aciki yakeyi kafin mutane su fara cika wurin daya bayan daya wurin ya cika.

   Bayan an idar da sallah ya jima yana addua bai fargaba  ashe daga shi sai wanan tsohon a zaune a lokaci kusan daya suka mike kowa ya nufi hanyar fita.

    Amadi ya riga dattijon fitowa saidai a yadda yanayin tsohon yake tafiya yasa Amadin tausaya mai ta hanyar dauko mashi takalman shi da yawan jama,a yasa suka turashi nisa ya dauko ya daidaita mashi ta yadda zaiji saukin sakawa a kafanshi.

   Kafadanshi yaji andafa ana mai addu,a ya amsa da amin tare da dagowa yanawa tsohon godiya ta hanyan dan ja da baya kadan har lokacin daya daidaita ya saka takalman nasa.

   Ganin sun sauka daga dan steps din masallacin ya dan juyo yana fadin nagode baba Allah ya bamu wuni mai albarka sai baiga kowa a wurin ba shi a zaton shi tson yabi ta baya ya wucene a cikin duhu don wurin babu haske sosai don haka yasa kai yawuce zuwa gida.

   Sannu sannu yake jin kamar sanyi a jikin shi kwanciya a wanan lokacin ba halinshi bane amma sai yadan kishingida kafin gari ya ida wayewa.

   Mafalkin dayayine ya sashi tashi a firgice Dije ce tsaye a kanshi tana tayar dashi daga barcin ya amsa da na,am tace lafiya kake kuwa yau har wanan lokacin baka fito zuwa daukan karatun kaba ?

   Mikewa yayi yana mika gami da salati yana fadin wallahi sanyine naji lokaci guda na dan kwanta ashe barci ya daukeni ban sani ba a haka.

   Tashi ka gagauta ka shirya kafita kasan halin matar nan da kake aiki a karkashinta da fitinan tsiya kada kaje yauma ta hanaka kudin aikin ka ga kudin nan na jiya sai kayi amfani dashi.

   Ki barshi Dije zanyi sauri na karasa da kafa insha Allahu zan isa da wuri ya fada yana jawo tufafin shi dake rataye akusa ta dan tsaya tsaye sagale da hannu da kudin tana mamaki  halin jikan nata.

    Tausayin shi take yadda shima yake tausayinta saidai basu da dabara sai addua a tsakanin su don talaucin da yai masu katutu a rayuwan su banda dan gidan nan da uwar garke da yayan ta hudu yanzu da suka mallaka basu da komai a rayuwansu sai hamdala ga ubangiji.

    Duk saurin da yayi kamar zai tashi sama ga jikin yana dan jin shi hakan bai hanashi makara ga aikin shi da yankan fara yiba kafin ya shiga class.

   Don har madam ta bar sakin cewa idan yazo ace dashi ya wuce kawai bata so yana zuwa yarinyar shagon ta tare shi tana tsugunta mashi jin haka yasa yayi kwana zuwa department din su.

    A dadafe ranan ya dauki darasin shi saidai ga dawo dole abin hawa ya nema ya dawo dashi gida yana kokarin ciro dan dari biyun daya kwana kusan bakwai cikin aljihunshi yana boyom shi yaji mai acaban yace dashi barshi kawai taimaka maka nayi aini ba haya nakeyi ba dama na kawo wani wurin.

   Godiya ya fara mai kafin shikan yaja mashin din shi ya tafi shi kuma yasa kai ya shige cikin gidan a kasalance daganin shi kasan jikin shi ba daidai yake maiba a ranan.

   Don shi mutum ne mai kazar kazar da zafin nama don yana amfani da karfin shi da kiran da Allah yai mashi na masi karfi a jika.

     Haka na wuni a kwance inbanda ruwan tea din da ummah ta matsa min nasha da safe babu komai a cikin cikina mama kuma tunda ta tafi bata kara lekowa part din mu ba da sunan dubani.

   Ummah ce ke faman zaraya a kaina har saida taga na dan samu sauki zuwa yamma na zauna ta dan rage lekoni a dakin .

  Allah da ikkn shi a wanan yammacin Abbam mu ya dawo daga Abuja kowa na zuwa falon shi gaidashi don haka sabian gidan mu yake .

   Saidai har yara suka gama zuwa baiga nazo na gaida shi ba yasa ya tambays ina mamata take ne banga giccinta ba a nan wani irin kawar da kai mama tayi gefe daya tana fadin tana part dinsu mana.

   Lafiya take kuwa ya sake tambaya a lokacin da ummah ke shigowa dauke da abinci don taron shi duk da basu san da dawowanshi ba a ranan amma bai rasa abinda zai ciba wanda zai saka a cikin shi.

    Wai maamah yake tambaya ta fada dana wani dan cicika she wai fushi mamakeyi a rana wai Abba ya dawo ranan girkin mama saboda haka an munafurceta ke nan shi da ummah.

   Ina mamata ya tambayi ummah yana fadin naga kowa yazo gaidani bangata ba tun dazun ya tambaya yana tsure ummah da idon jin amsan da zata bashi.

    Saida ta kalli mama take fadin tana daki bata da lafiya tun jiya take fama da ciwon kai dazun ma saida na kaita asibiti da safe da kan ya matsa mata.

  Subbahanallahi shine ba a fada min ba yanzu an samu magani ya tsaya ko ya fada yana saukowa daga saman kujeran da yake  zaune a kai don yaji dadin cin abincin da zaici.

   Kallon mama yayi yana fadin hjy maimuna amma baki fada min ba ai dana kira dazun to ai naga uwarta ta kaita asibiti ko ta fada a dan tsiwace.

    Murmushi Abbacdin yayi yana fadin yau kuma salmace uwarta cikin zolaya ta juyo fuska daure tana fadin uwartane mana tunda takaita ina gidan nan nima banda labarin hakan.

    Ai ina na fada maki dalilin kaita tun dazun bawai na kaita da wani manufa bane wallahi naga dai za a takura makune kawai.

    Ni bashi ba yaya jikin nata yake yanzu Abban ya tambaya tana kallon fuskan ummah din yasa in ya kallo mama abinda zai samu a wurinta.

 

No comments