Breaking News

TUMFAFIYA 26

 

 


 

 

ZAINAB IDRIS MAKAWA [1/24, 8:34 PM] +234 706 815 1331: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA SIRIN KI     SAI ALLAH  ,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

 2️⃣6️⃣

ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,

 

   Ina uwargida da Amaren gida dama sarakan gida da kowa na gida muna maiba da hakkuri ga kowa dake jin ana fadan halin matsayin da yake a gida.

   Uwargida sunce an soki matsayin su an rage masu GP amaren ma sukace ana fa yawan aza masu laifi hakama uwayen gida sarakan gida sun fadi korafin su.

   To yar uwa rigace ta zamani abin yayi idan ke hakan ba halinki bane hslin waccan ce ko halin wanan don abinda yafi yawa a yanzu ne muke fada a fili.

   Uwargida za a karo kishiya tace shigo zaki sameni ciki ai haka amaryan zamani da danmara a kwankwason ta take shigowa uwargida yanzu saidai kowa dabaran shi da rikon Allah ya fitar dashi.

  Bana bayan kowa don kowa nawane a cikin don haka muyi nishadi mu karu da juna ta wani fannin don ace zomu zauna zo mu saba Allah yasa mufi karfin zukatan mu muyi kishi daidai da imanin mu amin nagode nagoda da bin novel dina ko wani lokaci.

    Zufa take karyawa daga zaunen kafin ta tattaro zuciyan ta wuri daya ta samu natsuwa ta dauki hakan da sherin mafalkine ba wai zai faru a gaske ba.

    Jin budan kofan jikan nata har shigan shi dan makewayin su ya fito duk a kunnen Dije da jinsa ya fito dags bandakin yasata bude kofan ta a lokacin da yai daidai da muryan Amadin dake fadin waye a wurin nan ne wai tsugune ?

    Dije dake fitowa ta amsa da ina kuma yace daga barin katangan can kamar mutum yana zaune a wurin da sauri ta koma dakinta ta dauko toci tana kokarin kunnawa zuwa lokacin har Amadin ya mike ya kusa kai saitin wurin da lalube don ganin ko waye ?

    A lokacin Dije ta hasko tocilanta a wurin ja yayi ya tsaya wuri daya yana jan tsuki tare da fadin ashe dan icen nan nefa yayi girma haka har nake ganin innuwanshi kamar na mutum a wurin.

    Ya juyo ya koma inda yake duke da farko da shirin alwala Dije da ta shige bandakin ta fito ta samu zai fice zuwa masallaci tayi mai a dawo lafiya.

  Ya amsa a gurguje ya fice daga gidan har cikin lokacin akwai sauran asubahi don haka akwai sauran duhu sosai gari bai gama washewa ba a lokacin.

    Kai ta dago daga inda take zaunen ta kalli wurin da Amadin ya kalla abinda yagani ta ganowa idonta itama don mutum sak ta gani a wajen duke.

    Gaban Dije ne ya fadi dam lokaci guda don abinda idonta ya gano mata din a lokacin sauri Dije tayi ta mike a daidai lokacin uwargarke ta saka kuka acikin muryan data kwana biyu batayishi ba a gidan.

    Tun wanan lokacin wanan akuyan bata sauta kukanta ba haka take tsaye tana wani irin kuka sauran dabbobin kuma suna tsaye suna kallon ta yayin da kunnuwan su yake wani irin dage da alaman wani abin tsoro suka gani lokacin ya gitta.

   Har Amadi ya dawo daga sallah suna a hakan wurin su ya nufa ya zagaya su ya dan duduba ko maciji suka gani don suna hakan idan dabbobi sunga wani abin cutarwa garesu.

   Zasu dauki kuka sosai suna nuna alaman hakan saidai hakan yana da wuya a iya gane hakan idan ba mutum ya kwarai a kiyo yayi sabo da dabban zai iya fahinta idan ta shiga cikin bakon yanayi.

   Share wurin yayi ya debo masu abinci ya canza ruwan shansu ya dan juya zaibar wurin a lokacin uwargarken ta dona kanta tsakankanin shi zakace tana susan kantane ajikin nasa a lokacin.

   Kiyi hakkuri uwargarke kuci wanan dusa yau in sha Allahu zan sayo maku abinci idan zan dawo kuci wanan din ku koshi kafin na dawo yana dan ture kanta daga jikinshi.

   Buta ya dauka ya cika da ruwa ya nufi bandaki ya watso ruwa don haka al,adanshi yake bai tsaya yayi wanka yadda ya kamata sai ranan jumma,a zai tsaya yayi wankan arziki ya gyara jikinshi ya fito mutum sak sai ko sallah bana da yayi kokari ya dinka kala biyu koshi da dalilin yin hakan a zuciyarshi.

   Kananan kaya ya saka a jikin shi ya dauki dan jakkar da yake saka takardun shi ya fito bai tsaya wani duban ko shigar tasa tayi ba ya fito daga dakin.

   Dakin Dije ya nufa tun kan ya karaso ya fara kwalawa Dijen kira yana fadin Dije ni zan shiga school kin san yau zamu koma makaranta .

  Yaka Amadi muyi magana dije ta fada cikin tausasa murya yace wallahi Dije na makara yau din nan kinsan yau aka koma daga hutun sallah gani a gida har wanan lokacin zam iya zuwa na samu har an zauna.

   Saina dawo Dije muyi maganan koma meye ya fada ya fara tafiya don barin wurin binshi tayi da kallo dama tasan kota fada mai abinda ke zuciyata din ba lalai bane ya yarda da ita don kasancewar shi dan boko yaro kuma.

   Hakan ya tafi ya barta da mamakin shi na rashin tsayawan shi suyi zancen da take son yi dashi din gaba daya ta kasa gane kanshi cikin kwanakin nan.

    Abubuwa yakeyi kamar wani abu yana damun rayuwan shi yana boye hakan gareta dkn duk da bai da hayaniya dama sai miskilanci amma yana dan sakin jiki ya fada mata damuwan shi a baya.

 Amma yanzu sam baida lokacin tsayawa yin hakan sai ya nuna ko yaushe kamar a uzurce yake a yanzu din.

     Har nayi sallama da ummah na kama hanyar fita daga part din mu muryan ummah ya tsayar dani lokaci guda na juyo ina fuskantan ummah din.

   Maamah kin dai san abinda mahaifinku ya fada maki don haka ki kula ki kama kanki a duk inda kikaje don kimarki itace darajan ki ki kama kanki na fada maki.

 Kwalkwal nayi da idona don ina jin dacin wanan kalman a zuciya nasan kuma mahaifiyata tafini jin hakan sosai a ranta dannewa kawai takeyi kada a gane hakan.

   Na iya bude bakina da kyar nace ummah zan kula in sha Allah nasa kai na fita wurin motana na nufa saida na tsaya na dan duba motan don hango scratch a jikin motan danayi tun daga nisa wanda ni bansan dashi ba a lokacin.

   Ban koma ciki ba na daure na fice hakana zuciya ba dadi har lokacin ga tunanen zancen iyayyena yanzu kuma na rasa wanda ya gogar min motana.

   To waye yai min haka da motar nawa don tunda akai sallah ban fito ba lafiya kalau na aje motana kuma yanzu na samu hakan a jikinta.

   Na shiga school a kan lokaci don haka na fito ina dan waige waigen satan kallon inda na saba tarardashi muke haduwa saidai a fakaice nake satan kallon wurin don kada na gashi kamar yadda muka saba din.

   Nayi mamakin ganin hakan har na shiga building din mu na zauna a tsarge kowa ka gani aranan yasha kwalliya a cikin tufafi masu kyau don adon sallah.

   Kaina dukar saman table din dake gabana ina tuno abubuwa da dama naji an dafa min kafadana na dago da sauri ina kallon maishi Hannatu ce a tsaye take min murmushi kafin ta zagayo ta dauke jakkar dana aje a wurin.

   Ta zauna take fadin wai zahra idon ki ke nan dama wallahi zahra baki da kirki ace wai ayi sallah bakijini ba kuma baki nemeni ba kinji ko lafiya nake ba.

   Kaina dago ina murmushi a gajarce nace haba Hannatu ko kallona kikayi ai zaki fahinci bana cikin dadin rai a tare dani yanzu don jikina na bani cewa har karamin rama nayi.

   Kallon tsab tayi min kafin tace gaskine hakan kuma to meke faruwa na kalleta ina hade bakin ciki a cikina nace sallah nan ciwo nayi saidai bai kaini kwance bane.

   Lectura ne ya shigo ya katse muna hira  mu kowa ya samu wuri ya natsu aka fara lecture bamu samu kan mu ba sai karfe daya muka fito don break da za aje na sallah.

   Hanya na canza hannatu ta kalloni tana mamaki bata da zabi sai bina da tayi muka isa wurin sallah baya  mun idar ne wayana ya dauki karan kira lokaci guda.

    Ban dauka ba don ganin wanda ke kiran nawa manir ne nasan kuma zancen karatu zai min don ko na dauka ban san amsan da zan iya bashi ba lokacin don haka naki daukan wayan karshema daukan wayan nayi na sashi a silent.

 Ganin hakan yasa ya kira layin hannatu ta dauka tambayanta yayi idan muna tarene tace dashi gamu cikin mosque.

   Ba zaku fito muje lesson bane yau ko baku gama hutun sallah bane ku har yanzu don shi dama sarkin barkwancine ko yaushe.

    Kashe wayan tayi tana kallona tare da fadin Mayana mufa ake jira akace wurin lesson kada mu bata masu lokaci.

   Ba zan samu zuwa lesson ba na bata amsa kai tsaye har yanzu jikin ke damun kine ta tambayeni nace eh kije kawai zan dan kwanta a nan cikin mosque kafin ku karasa.

    Bataso zuwa ba don ganin banje ba amma na nuna mata ba komai ga zuwan nata don kada mutaru duka  bamu je sai ta tashi ta mike ta fita sai dai da gani tana a cikin kwankwanto a lokacin.

   Fitan ta nakai kwance kasan kafet din dake malale cikin mosqu din ina lumshe idanuna zaka dauka ko barci nakeyi a lokacin.

   Tan isa kafin ta karaso manir yace ina ita kuma yar mulkin ko tana tafe ne mu cigaba ?

   Fuskata ta dan bata kafin tace ina ganin zahra bata da lafiya don ko a class kusan haka na sameta a kwance dana shigo let start don nasan dama ba zata zo ba ya fada cikin wani yanayi.

  Ok master yana da masaniyar rashin zuwan ta ke nan baidai bashi amsa ba ya fara gaidasu da dawowa daga sallah kafin su fara darasin.

    Har suka kai lokacin da muke tashi yayi masu sallama ya tafi a karshe muka koma aji aka tashi na nufi gida haka muka dinga yi har sati ya shige suka fara fahintar cewa akwai matsala a tsakanin mune.

  Gashi kuma har ranan bamu hadu dashi ba kuma ban fasa satab kallon wurin ba duk na iso zanyi kokari na juya na kalla ko yana wurin saidai ban ganin kowa.

   Sati biyu muna hakan har kowa ya gama fahintar komai ranan monday bayan mun fito daga daukan karatune hannatu ta tutsiyeni da tambayan dalilin rashin zuwana group discussion a yan kwanakin nan ?

   Ba komai kawai na daina hakan ne don nima na koyi fahinta daga malami da kaina wani irin kallo tayi min ta sake murmushi tare da fadin.

   Zahra kenan kina ganin a dan zaman mu tare a school din nan ba zan iya fahintar halinda kike ciki ba ke bake bafa har su manir da sauran su ina iya fahintar yanayin su suma maza.

   Nasha zaki fada min don muga ko za a iya walwale matsalan a cikin sauki duk da daga ke har master din kuna kokarin boye muna cewa babu komai a tsakanin ku.

   Umhumm hannatu ki bari kawai wanan zancen ya wuce nake gani don ina kokarin mantawa da komai kan wanan zancen.

   Zahra kina ganin cewa ku bata tsakanin ki da master shine mafita a gareki ko me kifa sani irin su master tsada sukeyi yanzu a cikin maza.

  Ko kin san yawan yan matan school din nan da suke son kasancewa dashi  amma yaki bada daman hakan,  ni wallahi dama ganin yanayin sa idan badon naga gidansu ba sai nace shi din dan gidan wasu manyan mutane ne sosai a garin nan.

   To amma kuma nasan shi har irin sana,anshi sai hakan ya fara sani a kwankwanto a kanshi kuma yanzu dai ba wanan nan bama zahra meya kawo matsala a tsakanin ku ?

    Kamar bansan tana magana ba don hankalina na mayar a wayana ina duba ban dago kai gareta ba naji tace to shike nan yanzun na fahinci irin zaman da mukeyi da juna dake duk da kece kika daukeni hakan.

  Don ni tsakanina da Allah nake zaman arziki dake ba don wani abuba can zarah amma naga ke ba haka  kika daukeni ba ke har yanzu.

  Nan nake kawo maki korafin yayata dake tasheni ki bani shawara in kuma je inyi amfani da shawaran naki yai min amfani a karshe.

   Kaina dago na kalleta a cikin yanayin tausayin kaina nace hannatu ba hakana bane matsala aka samu an fadawa Abbana cewa wai soyayya muke da Ahmed shine Abbana yai min iyakan tsayawa dashi.

   Abba fa har wanan zancen yakai kunnen Abban ku kai mutane basu da kyau yanzu shiyasa wasu ke fadin anbar kiwon dabbobi a yanzu an koma kiwon mutane.

   Ba wanan ba hannatu Abba har Ahmed din ya kira yai mashi iyaka dani ya kumaci zarafin shi a kaina da wani ido zan kalli Ahmed a yanzu kike gani.

  Ke kanki Hannatu kinsa Ahmed kadai ke min bayani na fahinci abinda darasi ya kumsa na gane yanzun kuma Abba yaci mashi mutunci kan haka, har yana fadin cewa Ahmed baida asali .

  What ta fada da dan karfi tana kallona kafin tace min kuma shi Ahmed din yasan da wanan zancen bansan koya fada mashi ba daya kirashi din.

   Zahra ki bar wanan zancen don Allah mu bari sai mun samu lokaci mu zauna asan yadda za a bullowa lamarin sai dai ban zaton ya fadi hakan a gaban shi Ahmed din ai.

   Nima shine tsorona don nasan halin Abba zai iya fadin komai ko a gabanshi idan ranshi ya baci tunda acewa Abban soyayya mukeyi nida Ahmed din ba karatu ba.

   Amma ke baki ganin rashin kyautawan ki ga hakan aisai ya zata kema hakan da Abban yai mashi bai dameki bane kamata yayi mu sameshi mu bashi hakkuri .

  Kinga a nan zamuji shin Abba ya fada mashi maganganu marasa dadin kamar yadda ya fada maki ni gaskiya kamar hanyar daya dace ke nan mubi nake gani.

   Hannutu kunyanshi gaba daya nake ji a yanzu bazan boye maki ba kan wanan maganan wallahi nasa cewa ba karamin shakuwa ashe mukayi dashi ba.

   Don tun wanan ranan wallahi Hannatu na nemi farincikina na rashi a tare dani kullun jin kaina a cikin kinci nake kuma Abba har zai tafi ya kara jadda min cewa duk aka fada mai cewa angani tare dashi zai dauki mumunan mataki a kaina ranan .

   Wanan yasa nake matukar tsoron fita har mu hadu din dashi wani dan gulma yaje kuma ya fadawa Abba kinsan Abba ba zai raga min ba idan har yaji hakan.

  Gaskiyane ki dai bari gobe idan nayi tunane kan yadds zamu bullowa zancen sai mu san abin yi don gaskiya ban baki shawaran barin wanan guy din ba zahra.

  Murmushi nayi tare da fadin wai meyasa mutane ke yawan dauka muna soyayya da Ahmed ne, mutuncine fa kawai a tsakanin mu kema kin sani.

. Nikan ban yarda da wanan maganan ba ga kowan ku donko makaho ya laluba yasan gaskiya  kedai kawai mubar zancen sai gobe in sha Allahu.

    Ina hanya komawa gida wayana yayi ringing na mika hannu na dauka daga gefena ya musa ne a layin da murnana na dauki wayan ina gaidashi.

   Zahran mama ke nan ya fada na lumshe idona don tunawa da wanan sunan da suke kirana dashi shida ya jafar yace yanzu kin zama busy ko neman mutane bakyayi ki gaidasu.

    No wallahi yaya ba hakana bane yace to ya ne Allah karatune yanzu yai min yawa sam banda lokacin kaina ga komai yanzu.

   Saina soyayya da yan uwanki dalibai ko Zahra Abba ya kawo min karanki yace kin fara soyayya da wani karamin yaro dan karamin gida a school din ku.

   Wallahi ya ba hakana bane na fada ina samun wuri na parker motar na kwashe komai daya faru na fada mashi har mutuncin dake tsakanina da Ahmed din da dan sabon da nayi dashi fiye da kowa a school din.

  Bayan ya gama saurarena yace min kin gane zahra ki janye duk wani alaka tsakanin ki da kowa yanzu kiyi facing din studies din ki kamar yadda Abba yake son kiyi.

 Shawara sosai ya bani kafin mu kashe waya bayan munyi sallama na tayar da motar na karasa gida ina tunane don ni abubuwan ma sun min yawa a yanzu nake gani.

    Ranan banyi barcin kirki ba ina faman tunanen maganganun ya musa dana hannatu a raina sai kullawa nake ina walwalewa ni kadai a dakin nawa .

   Washegari na tashi sukuku dani nagama shirin da zanyi na fice a gidan tunda safe na samu malamin yazo bai shiga ajin ba don haka kusan tare dashi muka shiga.

   Sai bayan gama lectures din ne hannatu taso muyi maganan jiya din sai ya kasance kaina yana dan sara min muna fita maimakon mu wuce zuwa mosque sai cewa nayi da hannatun kaina ke min ciwo zanje gida insha magani in kwanta.

   Kallon mamaki take min din muna da lecte karfe biyu da rabi ganin da gaske nake yasa ta kyaleni in tafi din na nufi wurin motana nadan duka ina bude motan naji muryan shi abayana yana fadin

No comments